Babban Labari

Rikici da Ɗangote ya ci kujerar shugaban NMDPRA

Rikici da Ɗangote ya ci kujerar shugaban NMDPRA

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Abu kamar wasa, amma sai rikici tsakanin Shugaban rukunin kamfanonin ɗangote, Alhaji Aliko ɗangote, da Shugaban Hukumar Kula da Haƙowa da Tace Man Fetur ta Nijeriya (NMDPRA), Malam Farouk Ahmed, ya kai ga cin kujerar shugaban na hukumar ta NMDPRA. Tun da fari dai ɗangote ya yi kira ga hukumomin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da su gudanar da cikakken bincike kan zargin da ake yi wa Shugaban Hukumar Kula da Haƙowa da Tace Man Fetur ta Nijeriya (NMDPRA), Malam Farouk Ahmed, kan biyan kuɗin karatun ’ya’yansa a ƙasar Switzerland da ya kai kimanin dala miliyan biyar. Dangote…
Read More
Yadda tirela ta halaka ɗaliban Jami’ar Jos takwas

Yadda tirela ta halaka ɗaliban Jami’ar Jos takwas

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Mutane sun shiga firgici da ɗimuwa a safiyar jiya Alhamis, 11 ga Disamba, 2025, bayan hatsarin mota mai tsanani da ya yi ajalin ɗaliban Jami’ar Jos (UNIJOS) takwas tare da direban motarsu akan titin Zariya da yake cikin garin Jos, Babban Birnin Jihar Filato. Shaidu sun ce, hatsarin ya faru ne a lokacin da wata babbar mota ƙirar tirela, wacce ake zaton ta samu matsalar birki, ta ƙwace wa direban ta bugi ɗaya daga cikin motoci biyu da ɗaliban suka ɗauka, domin zuwa yawon dare. Sai bugun ya fasa motar gabaɗaya tare da jefa ta kai…
Read More
Katsina: Mai ciki ta rasu bisa ƙin karɓar ‘transfer’

Katsina: Mai ciki ta rasu bisa ƙin karɓar ‘transfer’

Daga UMAR GARBA a Katsina Wata mata mai juna biyu, Aisha Najamu, ta rasa ranta a asibitin Turai Umaru Musa Yar’Adua da ke Katsina bayan ma’aikatan asibitin sun ƙi karɓar kuɗin iskar ‘oxygen’ ta hanyar tura kuɗi ta yanbar gizo (wato transfer), inda suka dage cewa sai an biya kuɗi a hannu (cash) kafin a ba ta agajin gaggawa. Hakan ya sa matar har ta mutu, bisa jinkirin saka mata iskar da asibitin ta ƙi yi, don ba su zo da kuɗi a hannu ba. Lamarin, wanda ya faru ne a ranar Laraba da daddare, shaidun gani da ido sun…
Read More
Marigayi Sheikh Ɗahiru Bauchi (1927 – 2025)

Marigayi Sheikh Ɗahiru Bauchi (1927 – 2025)

*Rasuwarsa, tarihinsa, iyalinsa da nasarorinsa *Sarkin Musulmi ya jagoranci yi masa addu'a ta musamman *Tinubu, gwamnatin Bauchi, JIBWIS da sauran al’umma sun nuna juyayinsu Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Al'ummar Musulmi a Nijeriya da ƙasashe maƙota suna ci gaba da alhinin rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci kuma jagoran ɗariƙar Tijjaniya, Sheikh ɗahiru Usman Bauchi bayan shafe shekaru kusan 100 a duniya. Rahotanni sun bayyana cewa, fitaccen malamin ya rasu ne a daren Laraba, wayewar Alhamis, lamarin da ya kawo ƙarshen jagorancinsa na miliyoyin al’umma a Nijeriya da ma ƙasashen waje. A ranar 28 ga Yuni, 1927 aka haifi shehin…
Read More
An yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai-da-rai

An yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai-da-rai

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa shugaban masu fafutikar kafar ƙasar Biyafara (IPOB), Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai. Wannan ya biyo bayan hukuncin da Mai Shari'a James Omotosho ya yanke a ranar Alhamis, 20 ga Nuwamba, 2025. A cewar alƙalin, "wanda aka yanke wa hukuncin bai yi abin da ya dace ba a duk lokacin zaman kotun, yana mai jaddada cewa ya jawo tsaiko a shari'ar. Ya ƙara da cewa kotun ba za ta yi la'akari da raini da shugaban IPOB ɗin ya yi a kotu yayin da yake…
Read More
Tsadar rayuwa yana durƙusar da kafafen yaɗa labarai

Tsadar rayuwa yana durƙusar da kafafen yaɗa labarai

*Tinubu ya amince da rangwamen haraji ga gidajen jarida *Gwamnatin Tarayya ba ta tsangwamar manema labarai, inji Idris Daga SANI AHMAD GIWA da MAHDI MUSA MUH’D Shugaban ƙungiyar Editocin Nijeriya (NGE), Kwamred Eze Anaba, ya koka kan yadda tsadar rayuwa da matsin tattalin arziki suke hana kafafen yaɗa labarai gudanar da aikinsu yadda ya kamata, yana mai roƙon Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakan tallafi, don ceto masana’antar da ke fuskantar barazanar rushewa. Yayin da yake jawabi a taron shekara-shekara na 21 na ƙungiyar Editoci ta Nijeriya (ANEC), wanda aka gudanar a Dakin Taron Fadar Shugaban ƙasa a Abuja, Anaba ya…
Read More
Zargin kashe Kiristoci: Ana ci gaba da yin tir da Trump

Zargin kashe Kiristoci: Ana ci gaba da yin tir da Trump

*Tinubu, ECOWAS, Chana, Gumi da rahoton BBC lauyan Amurka sun yi allawadai *An yi musayar yawu tsakanin Akpabio da Barau  Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Tarayyar NIjeriya ta bayyana rashin jin daɗinta kan matakin da Gwamnatin ƙasar Amurka ta ɗauka na sanya Nijeriya cikin jerin ƙasashen da ake ganin suna take ’yancin yin addini. Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na ƙasa, Mohammed Idris (FNIPR), ne ya bayyana haka yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a Cibiyar ƙasa ta Yaɗa Labarai, Abuja, a ranar Laraba, 5 ga Nuwamba, 2025. Idris ya ce gwamnatin Nijeriya ta…
Read More
Zugar Shaiɗan ce ta kama Maryam Sanda – Gumi

Zugar Shaiɗan ce ta kama Maryam Sanda – Gumi

*Ya yi maraba da rage ma ta hukunci Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shahararren malamin addinin Musulunci, Shaikh Ahmad Gumi, ya yi maraba da sauya wa Maryam Sanda hukunci daga kisa zuwa zaman shekaru 12 a gidan yari, yana mai cewa nadamar da ta nuna bayan kisan mijinta alama ce ta “aikin Shaiɗan”. Shaikh Gumi ya bayyana haka a wani saƙon da ya wallafa a Facebook, inda ya ce kisan mijin nata, Bilyaminu Bello, ya faru ne da tsananin fushi da tasirin Shaiɗan, sannan kuma ta fashe da kuka bayan ta gane abin da ta aikata — abin da ya kira…
Read More
Za a yi gumurzu a zaɓen 2027 – Kwankwaso

Za a yi gumurzu a zaɓen 2027 – Kwankwaso

*A shirye muke mu yi haɗaka, inji shi Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma ɗan takarar kujerar Shugaban ƙasa na jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) a zaɓen 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi hasashen cewa zaɓen 2027 zai kasance mafi tsanani a tarihin dimokuraɗiyyar Nijeriya, kamar yadda ya bayyana cewa jam’iyyarsa a shirye take ta ƙulla ƙawance da sauran jam’iyyun siyasa ciki har da shugaban ƙasa Bola Tinubu da Peter Obi na jam’iyyar Labour. Da yake magana a wata hira da BBC Hausa da Blueprint Manhaja ta sa ido, Kwankwaso, wanda a kwanan…
Read More
Ana sake duba yafiyar su Maryam Sanda

Ana sake duba yafiyar su Maryam Sanda

*Ministan Shari’a ya yi ƙarin haske kan yafiyar Tinubu ga wasu fursunonin Nijeriya Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta yi ƙarin hasken cewa, babu wani fursuna da aka saki sakamakon yafiya da Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi musu a kwanakin baya lokacin bikin ’Yancin Kai, ciki kuwa har da Maryam Sanda, wacce ta kashe mijinta, Bilyaminu Bello. Wannan bayanin ya fito ne daga bakin Ministan Shari’a kuma Antoni Janar na Tarayya, Lateef Fagbemi (SAN), a cikin wata sanarwa jiya Alhamis, yayin da ƙorafi ya yi yawa biyo bayan sakin jerin sunayen mutum 82 da…
Read More