Ra’ayi

Shin ‘yan ta’adda sun fi ƙarfin jami’an tsaronmu ne?

Shin ‘yan ta’adda sun fi ƙarfin jami’an tsaronmu ne?

Daga SALMAN MUKHTAR A kwanakin baya an kai hare-hare guda biyu da suka ɗauki hankalin mutanen Najeriya, waɗanda sun ƙara fito da asalin ƙarfin 'yan ta'adda da kuma nuna yatsa ga ƙarfin jami'anmu. Hari na farko, shi ne wanda aka kai gidan gyaran hali na Kuje (Abuja), inda waɗannan maciya amanar ƙasa su ka yi ta harbe-harbe tare da ɓalle wannan magarƙama, in da rahotanni suka nuna aƙalla kashi 90% na mutanen da ke ciki sun tsere. A cikin wanda aka nema aka rasa a wannan magarƙama, har da tsohon jami'in ɗan sanda, Abba Kyari, da ake tuhuma da laifin…
Read More
Arewa: Idan jifa ya wuce kanka, ya faɗa kan uban kowa!

Arewa: Idan jifa ya wuce kanka, ya faɗa kan uban kowa!

Daga MUKHTAR MUDI SIPIKIN Matuƙar 'yan Arewa suna kan wannan irin batu da fahimtar, ni in har zan amfana ko kuma in har na samu to kowa ya mutu, ko kuma in har na tsira to kowa ya hallaka, to Arewa za tai ta ganin abin baƙin ciki yau da gobe. Irin wannan tunanin ne ke sanya wasunmu ke bin azzaluman 'yan siyasa, saboda in har za su ba su kuɗi, to sauran al'umma su mutu.Har ka ji ana ihu ana cewa "Ruwan da ya dake ka shi ne ruwa" Irin wannan ne ke sanya ka ga mutane sun haɗa…
Read More
Wai me Buhari yake zuwa yi Daura?

Wai me Buhari yake zuwa yi Daura?

Daga RAHAMA ABDULMAJID Abin mamaki ne matuƙa yadda shugaba Buhari ya mayar da zuwa ƙauyensu yawon salla kamar wani rukuni na biyu a shika-shikan Musulunci. Ba zuwansa Salla ko ƙauyen ne ke ci min tuwo a kwarya ba, a'a yadda a matsayinsa na tsohon jami'in tsaro ya san tasirin nuna naƙasu ko jarumta na jagora a idon maƙiya, kuma aka sha shi ya warke a kan hakan. Amma sam taurin kai baya bari ya ɗauki darasi har a kan kansa balle waninsa. A watan Agusta na shekarar 1985, Mataimakin Shugaban Ƙasa ya tafi Hajji a matsayin Amirul Hajji inda ya…
Read More
Taimaka wa jami’an tsaro gano maɓoyar ɓata-gari

Taimaka wa jami’an tsaro gano maɓoyar ɓata-gari

Daga ABBA YAKUBU ABDULLAHI A yayin da na ke wannan rubutu rahotanni na bayyana cewa, kawo yanzu a na cigaba da gano wasu manyan masu aikata laifi da suka tsere daga gidan Gyara Halinka na Kuje da ya ke Abuja, Babban Birnin Tarayya, sakamakon harin da aka ɗora alhakin sa kan ƙungiyar 'yan ta'adda ta ISWAP, waɗanda aka ce sun je ne domin kuɓutar da wasu 'yan uwansu da ke tsare a gidan yarin su kimanin 64. Bayan waɗanda aka je kuvutarwa har da ƙarin wasu vata gari da suka yi amfani da wannan dama suka tsere. A sanarwar da…
Read More
Yayin da INEC ta tsawaita rajistar masu zaɓe…

Yayin da INEC ta tsawaita rajistar masu zaɓe…

An yi farin ciki sosai a Nijeriya biyo bayan matakin da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ɗauka na tsawaita aikin rijistar masu kaɗa ƙuri’a (CVR). Kamar yadda jadawalin INEC ɗin ya nuna, ya kamata a kawo ƙarshen rijistar masu kaɗa ƙuri’a ne a ranar 30 ga watan Yunin 2022. Sai dai kuma, ba da daɗewa ba ne aka yi ta yin tururuwa a cibiyoyin rajistar don neman yin rajista, lamarin da ya sa cibiyoyin cika da kuma sanya jami’an hukumar aiki ba dare ba rana. Akwai abubuwan da suka sa jinkiri yin rijista ga wasu ’yan…
Read More
Tsakanin ASUU da Gwamnatin Tarayya, wai waye yake ƙoƙarin kawo wa ɗalibai cikas?

Tsakanin ASUU da Gwamnatin Tarayya, wai waye yake ƙoƙarin kawo wa ɗalibai cikas?

Daga NAFI'U SALISU  Yajin aikin Malaman Jami’o’i ba sabon abu ba ne a Nijeriya, musamman a lokacin da ɗalibai ke ƙoƙarin kammala zangon karatu, ko kuma lokacin da ya kamata a ce sun kama karatun ka’in-da-na’in. Wannan wani al’amari ne da faruwarsa kan sosa rayuka da dama, a ciki har da na iyayen ɗaliban da ‘ya’yansu dake karatu a Jami’a. Hakazalika, a duk lokacin da aka ce Malaman Jami’o’i suna yajin aiki, a kan daɗe ana kai ruwa rana tsakaninsu da Gwamnatin Tarayya, wanda kuma daga bisani a kan samu maslaha a ɗinke bakin zaren domin ɗalibai su dawo makarantu…
Read More
A kiyaye amfani da addini don son zuciya

A kiyaye amfani da addini don son zuciya

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Nijeriya na daga cikin ƙasashen duniya na sahun farko da jama'ar ƙasar ta ke da son addini. Wata majiyar ma na cewa, Nijeriya ce ƙasar da mutanen ta ke da tsananin son al'amarin addini. Komai na 'yan Nijeriya sai ka samu addini a ciki, ko da kuwa a sautin ƙarar waya ne, sai ka fahimci ƙarar wayar Musulmi da ta wanda ba Musulmi ba. Muna nuna son junan mu saboda addini, mu taimaki bare saboda addini, mu gujewa ɗan uwa saboda addini. Akwai masu addini na tsakani da Allah, akwai 'yan na gada, 'yan son zuciya…
Read More
Me ya sa maza suke kasa sauke haƙƙin iyalansu?

Me ya sa maza suke kasa sauke haƙƙin iyalansu?

Daga AMINA YUSUF ALI Wai meye ma haƙƙoƙin da suke kan namiji na iyalinsa? Musulunci Addini ne wanda cikin hikima za a ga ya kawo dukkan wasu hukunce-hukunce na zamantakewa. Don haka zaman aure ma bai bar shi a baya ba. Ya tsara haƙƙoƙin mace da miji a aure. Kuma ya jaddada su a cikin Al-Ƙur'ani da hadisai, domin a samu daidaito da fahimtar juna. A cikin haƙƙin da aka ɗora wa mace babba daga ciki shi ne ta yi biyayyar aure. Ta bi mijinta sau da ƙafa tare da ƙauna da tausayawa. Sannan mace ita ke da haƙƙin kula…
Read More
Duniyar ce ta sauya ko mutanen cikinta?

Duniyar ce ta sauya ko mutanen cikinta?

Assalamu alaikum. Tarbiyyar yara a wannan lokacin ta wuce a ce iyaye ne kawai za su kula da ita, zamani ya zo na sauyin rayuwa, yara da manya kowa ya san kuɗi kuma ya san inda ake kashe su, savanin shekarun baya da muka samu labarin cewa wani sai ya haura shekaru goma sha biyar ba ya kashe kuɗi da kansa sai dai in aikensa aka yi sayen wani abu. A zamanin iyaye da kakanni ana rayuwa ne ba tare da dogon buri ko hangen wani ya fini ba, mutum mai wadata yana iya riƙe yaran maƙotansa da sauran yaran…
Read More
Garaɓasar ranar Arfa

Garaɓasar ranar Arfa

Wasu daga cikin yadda za ku tsara yin amfani da ranar Arafat kamar yadda ya da ce don cimma alfanu mai tarin yawa. Yin barci kaɗan a daren ranar Arafa.Tashi daga barci don yin salloli da sahur da niyyar ɗaukar azumin ranar Arafa.Sai yin sallar nafila raka’a biyu ko huɗu, sannan a tabbatar an yi adu’oi a yayin sujjada na samun duk alherin duniyar nan da na lahira, kar a manta a yi wa Allah godiya da Ya ba da ikon ganin wannan rana mai albarka wadda Allah (S.W.T) Ya ke bada alkhairai da yafiya ga al’umma ma su yawa.Kafin…
Read More